ZARGIN 'YAN HAMAYYA KAN SHARI'0'IN KOTONA DA KOKAWAR BUHARI

 Wannan maƙale ce da ke kawo muku muhimman batutuwan da suka faru a Najeriya cikin makon da muke bankwana da shi



A farkon wannan mako mai karewa ne babbar jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya, ta bayyana hukunce-hukuncen da kotunan ɗaukaka ƙara suka yi, inda suka ƙwace nasarar wasu gwamnoni a matsayin "karan-tsaye" ga dimokraɗiyya.


Jam'iyyar adawar na zargin APC mai mulkin Najeriya ne da "amfani da ƙarfin iko" wajen tanƙwara hukuncin kotunan, zargin da APC ta musanta.


"Shari'ar Najeriya ta zama kamar rawar 'yan mata yanzu; idan an yi gaba, sai a koma baya," in ji Mataimakin Sakataren PDP na Ƙasa, Ibrahim Abdullahi.



Ya ce dalilan da mutanen nan ke gabatarwa suna kwace zaben nan, akasari batutuwan da suka shafi kafin zabe ne. A cewarsa, kotun koli ta yanke hukunci da cewa: "Ba abubuwa ba ne da suka shafe ta, a hukuncin da ta bayar kan dan takararmu, Atiku Abubakar".


Ya yi ikirarin cewa batun shari'ar, wata matsala da ka iya shafar daukacin nahiyar Afirka.


Mulkin ƴan Najeriya abu ne mai wahalar gaske - Buhari

Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ce ya mulki Najeriya da iyakar iyawar da Allah ya ba shi.


Buhari ya bayyana haka ne a tattaunawa da gidan talbijin na ƙasa (NTA). Sai dai ya ce ya bar wa mutane su yi alƙalancin ko ya yi ƙoƙari ko kuma akasin haka.



Tsohon shugaban ƙasar ya ce harkokin cikin gida sun dabaibaye gwamnatinsa, har ta kai ba ya damuwa da al'amuran ƙasashen waje a matsayinsa na shugaban ƙasa.


Ya ce babban ƙalubalen da ya fuskanta a lokacin mulkinsa, shi ne batun rashin tsaro da ya addabi ƙasar.


Sai dai, ya ce bayan ƙoƙari da gwamnatinsa ta yi wajen kyautata tsaro, hakan ya janyo mutane daga ciki da wajen ƙasar zuwa don zuba jari.


Fadar shugaban kasa ta yi watsi da sukar Obasanjo kan dimokuraɗiyya


Mahukunta da masana harkokin siyasa a Najeriya, na cigaba da tofa albarkacin bakinsu game da wani furuci da tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya yi cewa tsarin mulkin demokuradiyyar da aka ara daga ƙasashen yamma bai yi wa ƙasashen Afirka rana ba.


Tsohon shugaban Najeriyar ya soki tsarin yana cewa cewa ba ya la'akari da tarihin al'ummar Afirka da matsalolinsu, don haka akwai bukatar a maye shi da wani tsari na musamman.


Wasu dai na ganin cewa bai kamata ya kushe tsarin ba, kasancewar shi ne ya yi uwa da makarbiya wajen mayar da Najeriya kan turbar demokuradiyyar a shekarun baya.


Cif Olusegun Obansanjo wanda ya yi furucin a wani taron tattaunawa a kan dimokuraɗiyya a birnin Abeokuta ya ce tsarin dimokuraɗiyyar da aka ara daga ƙasashen yama musamman ma Amurka , tsari ne da ya yi hannun riga da matsalolin al'ummar Afrika saboda ba ya la'akari da tarihin nahiyar da kuma matsalolin al'umominta.


Don haka ne tsohon shugaban ya ce ya kamata al'umomin nahiyar su yi karatun ta natsu, su kirkiri wani tsarin mulki da zai dace da nahiyar.


Sai dai ga alama wannan furucin bai yi wa wasu dadi ba, ciki kuma har da mahukuta a Najeriya.


Takardun hukuncin shari'ar Kano sun tada jijiyoyin wuya

A ranar Larabar wannan mako mai karewa aka wayi gari cikin yanayi na ce-ce-ku-ce da tafka muhawara dangane da wani kwafin shari'ar da ke yawo a shafukan sada zumunta da ke nuna cewa kotun ɗauka ƙara ta bai wa gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf nasara a shari'ar da APC ke kalaubantarsa.


Tun bayan fitar kwafin shari'ar da ake cewa kotun ɗauka ƙara ce ta fitar kan hukuncin da ta yi kan zaɓen gwamnan, ake ta samun mabambanta ra'ayi musamman tsakanin ɓangarori biyun da ke cikin shari'ar.


Takardu da ke nuna cewa daga kotun suke - wadanda ke dauke da ƙunshin hukuncin suka zo da wani abu na bazata.Musamman a shafi na 67 na takardun hukuncin.


Wanna shafi na hukuncin ya yi matuƙar tayar da ƙura, inda magoya bayan NNPP da Abba Kabir Yusuf ke ganin hukuncin ya goyi bayansu, saɓanin abin da alƙalan kotun suka bayyana.


Lauyan jam'iyyar NNPP Barista Bashir Tudun Wazirci, ya ce wannan hukuncin ya nuna cewa kotun daukaka ƙara ta jingine hukuncin farko da kotun ɗaukaka ƙara ta yanke


A nata ɓangaren jam'iyyar APC ta bakin lauyanta, Barista Abdullahi Adamu Fagge ya ce su ba su samu takardun hukuncin a hukumance daga kotun ba.


Kotun ɗaukaka ƙara ta mayar wa Gwamna Sule na Nasarawa nasararsa

Kotun ɗaukaka ƙara da ke zaman ta a Abuja ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron ƙorafin zaɓen jihar Nasarawa, inda ta mayar wa Gwamna Abdullahi Sule nasara kamar yadda hukumar INEC ta bayyana a lokacin zaɓen gwamnan jihar na 2023.


A hukuncin da kotun ta yanke yau Alhamis, alƙalan kotun sun bayyana cewa kotun sauraron ƙorafin zaɓen gwamnan jihar Nasarawa ta yi kuskure a hukuncin da ta yanke.


A watan da ya gabata ne dai kotun sauraron ƙorafin zaɓen jihar Nassarawa ta soke nasarar gwamna Abdullahi Sule na jam'iyyar APC, tare da bayyana David Ombugadu na PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen na watan Maris ɗin 2023.


Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar wa Uba Sani nasara

Kotun ɗaukaka ƙara da ke zaman ta a Abuja ta tabbatar wa gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani nasara a zaɓen gwamnan jihar na 2023.


A hukuncin da ta zartar yau Juma’a, kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan takarar gwamnan jihar Kaduna na jam’iyyar PDP, Isa Ashiru ya shigar yana ƙalubalantar nasarar gwamnan na jihar Kaduna.


Tun farko, kotun sauraron ƙorafin zaɓe da ta zauna a Kaduna ta bayyana cewa Isa Ashiru ya gaza cika ƙa’ida game da lokacin shigar da ƙorafinsa na zaɓen gwamna, wanda hakan ya sanya ba za a iya amincewa da ƙorafinsa ba.


Sai dai an samu saɓani tsakanin alƙalan kotun, inda wasu daga cikin suka bayyana cewa akwai buƙatar sake zaɓe a wasu ƙananan hukumomi, in da Ashiru ya shigar da ƙara a kan lokaci.


Sai dai rashin gamsuwa da hukuncin kotun ya sanya dukkanin ƴan takarar biyu garzayawa kotu domin a tabbatar musu da nasara.


Kotun daukaka kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Nasir Idris

Kotun daukaka kara ta tabbatar da zaben Nasir Idris na ranar 18 ga watan Maris a matsayin halastaccen gwamnan jihar Kebbi.


Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ayarin alkalai guda uku da suka saurari shari'ar, sun yanke hukuncin cewa karar da dan takarar gwamnan Kebbi na jam'iyyar PDP, Janar Aminu Bande (mai ritaya) ya daukaka, ba ta da tushe.


A wani hukunci da alkalan dukkansu suka amince da shi karkashin jagorancin Mai shari'a Ndukwe Anyannwu, kotun daukaka karar ta cimma matsaya kan batutuwa guda biyar da Janar Bande ya shigar gabanta, inda ta bai wa Gwamna Nasir Idris gaskiya.


Mai shari'a Anyanwu ya cimma matsayin cewa masu kara ba su iya tabbatar da zarge-zargen da suka yi a kan takardar kammala karatu ta mataimakin gwamnan na jam'iyyar APC, Abubakar Umar Tafida ba kamar yadda doka ta tanada.


Al'amurra sun cabe a arewacin Najeriya — Babachir Lawal

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya a Najeriya, Babachir Lawal, ya ce zaben 2023 ya raba kan jama`a, musamman al`umar arewacin kasar, kuma da wuya yankin ya ci gajiyar siyasa idan al`umomin yankin ba su kawar da bambance-bambancen addini da kabilanci da ke tsakaninsu ba.


A hirarsa da BBC Mista Babachir Lawal, ya ce rarrabuwar ta yi kamarin da mafi yawan al`umma sun koma zaman-karofi sakamakon rashin yarda.


Babachir Lawal, ya ce,“Mu mun dade muna irin wannan kira a kan azo a hada kai amma ba a saurarenmu, shi ya sa ala tilas muka zama ‘yan kallo.“


Tsohon sakataren gwamnatin na Najeriya, ya ce duk abin da muka ce zai faru gashi nan yana faruwa muna gani.


Ya ce,“ Matsalar ita ce mutane ba sa ganin matsalar da ke damunsu, a don haka ni banga abin da za mu iya yi wa arewa ba don abin da ake gudu ya riga faru, musamman idan aka kalli irin halin da arewa ke ciki a Najeriya.“


Mista Babachir ya yi wadannan kalaman ne tare da yin kira a zo a hada kan arewa.


Ƴan bindiga na tursasa wa manoma biyan haraji kafin girbi a arewacin Najeriya

Manoma a yankin arewa maso yammacin Najeriya sun ce suna cikin halin tsaka mai wuya Sakamakon yadda 'yan bindiga suke hana garuruwa da dama na yankin yin girbi da kwashe kayan amfanin gona.


Manoman sun ce 'yan bindigar kan tilasta masu biyan zakkar amfanin gona da biyan kudi ko kuma idan ba haka ba su kwashe kayan amfanin gonar, ko su kone su kurmus.


Wani rahoto da hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya ce za a fuskanci a yunwa a arewacin Najeriya sakamakon matsaloli da suka kunshi har da tsaro a yankin.


Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce ta yi zama da shugabannin mutanen yankin kan yadda za a shawo kan matsalar tsaron.


Sojojin Nijeriya sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga da dama tare da kubutar da wasu a jihohin Kaduna da Neja

Rundunar sojin sama ta Najeriya ta yi nasarar kashe ‘yan bindiga da dama wadanda ke kai hare -hare da kuma satar mutane a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna da yankin karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna .


Ta ce ta kaddamar da farmakin ne domin kakkabe ‘yan bindigar da suka addabi yankin,


Kakakin rundunar sojin sama ta Najeriya Air Comodore Edward Gabkwet ya shaidawa BBC cewa :


“An kashe ‘yan fashin dajin ne a tsaunin Doka da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna”


Rundunar sojin sama ta Najeriya ta ce Bodari na cikin wadanda ‘yan fashin dajin da suka yi garkuwa da yara ‘yan makaranta a hanyar Abuja zuwa Kaduna.


Ma'aikata sama da 3000 da muka gada, ba su cancanci a dauke su aiki ba - Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano ta ce ta kammala aikin tantance dubban ma'aikatan da tsohuwar gwamnatin jiihar ta dauka a karshen wa'adin mulkinta, inda ta tabbatar da sama da mutum 9,000, a matsayin halastattu.


A bangare guda kuma ta ce ma’aikata 3,234 daga ciki, ta gano cewa ba su cika ka'idoji ba, don haka ta soke daukar su aiki.


Gwamnatin ta ce ta ɗauki wannan mataki ne bayan nazarin rahoton kwamitin da ya tantance ma’aikatan.


A farkon hawan Gwamna Abba Kabir Yusuf ne, ya ba da umarnin dakatar da ma’aikata fiye da 12,000 daga aiki, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce.

Comments

Popular posts from this blog

Wolverhampton Wanderers na son aron golan Arsenal Aaron Ramsdale mai shekara 27 a watan janairu tare da neman a sayar mata da shi a kaka mai zuwa.